fidelitybank

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Date:

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar a gaban kotu kan hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya, NMDPRA da kamfanin man fetur na Najeriya NNPCL, da kuma wasu kamfanonin mai guda biyar.

Ƙarar da aka shigar ta nemi waɗanda ake ƙara da su biya diyyar naira biliyan 100.

Ƙarar dai ta zargi NMDPRA da bayar da lasisin shigo da man fetur ba bisa ka’ida ba, wanda Dangote ya ce ya saɓa da dokar masana’antar man fetur ta 2021.

Sauran kamfanonin da aka kai ƙara sun haɗa da AYM Shafa da A.A. Rano da T. Time Petroleum, 2015 Petroleum da kuma Matrix Petroleum.

Dangote ya buƙaci kotu ta bayyana cewa NMDPRA ba ta tallafa wa matatun cikin gida yadda doka ta tanada ba.

Sai dai waɗanda aka kai ƙara sun mayar da martani cewa suna da cikakken cancantar karɓar lasisin, kuma Dangote na ƙoƙarin neman mamaye kasuwar man fetur a Najeriya ne gaba ɗaya.

A wata takarda da lauyoyin Dangote suka gabatar a kotu, sun bayyana cewa kamfanin ya yanke shawarar janye karar, ba tare da bayyana dalili ba.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp