fidelitybank

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Date:

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar a gaban kotu kan hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya, NMDPRA da kamfanin man fetur na Najeriya NNPCL, da kuma wasu kamfanonin mai guda biyar.

Ƙarar da aka shigar ta nemi waɗanda ake ƙara da su biya diyyar naira biliyan 100.

Ƙarar dai ta zargi NMDPRA da bayar da lasisin shigo da man fetur ba bisa ka’ida ba, wanda Dangote ya ce ya saɓa da dokar masana’antar man fetur ta 2021.

Sauran kamfanonin da aka kai ƙara sun haɗa da AYM Shafa da A.A. Rano da T. Time Petroleum, 2015 Petroleum da kuma Matrix Petroleum.

Dangote ya buƙaci kotu ta bayyana cewa NMDPRA ba ta tallafa wa matatun cikin gida yadda doka ta tanada ba.

Sai dai waɗanda aka kai ƙara sun mayar da martani cewa suna da cikakken cancantar karɓar lasisin, kuma Dangote na ƙoƙarin neman mamaye kasuwar man fetur a Najeriya ne gaba ɗaya.

A wata takarda da lauyoyin Dangote suka gabatar a kotu, sun bayyana cewa kamfanin ya yanke shawarar janye karar, ba tare da bayyana dalili ba.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp