fidelitybank

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Date:

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar a gaban kotu kan hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya, NMDPRA da kamfanin man fetur na Najeriya NNPCL, da kuma wasu kamfanonin mai guda biyar.

Ƙarar da aka shigar ta nemi waɗanda ake ƙara da su biya diyyar naira biliyan 100.

Ƙarar dai ta zargi NMDPRA da bayar da lasisin shigo da man fetur ba bisa ka’ida ba, wanda Dangote ya ce ya saɓa da dokar masana’antar man fetur ta 2021.

Sauran kamfanonin da aka kai ƙara sun haɗa da AYM Shafa da A.A. Rano da T. Time Petroleum, 2015 Petroleum da kuma Matrix Petroleum.

Dangote ya buƙaci kotu ta bayyana cewa NMDPRA ba ta tallafa wa matatun cikin gida yadda doka ta tanada ba.

Sai dai waɗanda aka kai ƙara sun mayar da martani cewa suna da cikakken cancantar karɓar lasisin, kuma Dangote na ƙoƙarin neman mamaye kasuwar man fetur a Najeriya ne gaba ɗaya.

A wata takarda da lauyoyin Dangote suka gabatar a kotu, sun bayyana cewa kamfanin ya yanke shawarar janye karar, ba tare da bayyana dalili ba.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp