Wani matashi da ake zargi da ƙwace wa wata mata waya a Kano ya rasa ransa sanadiyyar raunukan da ya samu bayan mota ta buge shi a lokacin da yake yunƙurin tserewa.
A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na facebook, mai magana da yawun ƴan sandan Najeriya a jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce mutumin ya rasu ne a yau Talata a sibitin Murtala da ke Kano.
A ranar Litinin rundunar ƴan sandan ta tabbatar da cewa wata mota ta kaɗe wani ɗan ƙwacen waya a titin zoo road da ke Kano.
Bayan haka ne aka garzaya da shi asibiti, inda aka tabbatar cewa ya samu karyewar kashin baya da kuma fashewar kai.


