Wani matashi maigadi wanda har yanzu ba a san sunansa ba, ya shiga hannun jami’an ‘yan sandan jihar Kano, sakamakon zarginsa da a ke yi da yaga littafi mai tsarki na Kur’ani tare da take wani sashinsa.
Wanda ake zargin, ya kubuta daga yunkurin babbaka shi da rai da jama’ar yankin Kuntau a birnin Kano suka yi niyya, bayan isar jami’an hukumar Hisbah wurin da lamarin ya faru a ranar Lahadi.
Daga bisani jami’an Hisbah sun mika shi hannun ‘yan sanda, kuma a halin yanzu an tsare shi inda ake ci gaba da bincike a kan shi.
Daily Trust ta rawaito cewa, wani É—an uwan mamallakin gidan da matashin ke gadi mai suna, Sunusi Ashiru, ya ce, da kyar matashin ya kubuta daga hannun jama’a.
Ya ce: “Ba na nan lokacin da ya aikata, amma na dawo na tarar da jama’a dauke da makamai daban-daban suna kokarin halaka shi. Na tambaya, sun yi min bayanin abinda ya yi, kuma a lokacin ne jami’an hukumar Hisbah suka kama shi tare da mika shi hannun ‘yan sanda.”
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da aukuwar lamarin, kuma ya ce, wanda ake zargin ya na hannun su tare da ci gaba da gudanar da bincike a kan shi.