fidelitybank

Matashin da ya yaga Kur’ani a Kano ya shiga hannun hukuma

Date:

Wani matashi maigadi wanda har yanzu ba a san sunansa ba, ya shiga hannun jami’an ‘yan sandan jihar Kano, sakamakon zarginsa da a ke yi da yaga littafi mai tsarki na Kur’ani tare da take wani sashinsa.

Wanda ake zargin, ya kubuta daga yunkurin babbaka shi da rai da jama’ar yankin Kuntau a birnin Kano suka yi niyya, bayan isar jami’an hukumar Hisbah wurin da lamarin ya faru a ranar Lahadi.

Daga bisani jami’an Hisbah sun mika shi hannun ‘yan sanda, kuma a halin yanzu an tsare shi inda ake ci gaba da bincike a kan shi.

Daily Trust ta rawaito cewa, wani É—an uwan mamallakin gidan da matashin ke gadi mai suna, Sunusi Ashiru, ya ce, da kyar matashin ya kubuta daga hannun jama’a.

Ya ce: “Ba na nan lokacin da ya aikata, amma na dawo na tarar da jama’a dauke da makamai daban-daban suna kokarin halaka shi. Na tambaya, sun yi min bayanin abinda ya yi, kuma a lokacin ne jami’an hukumar Hisbah suka kama shi tare da mika shi hannun ‘yan sanda.”

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da aukuwar lamarin, kuma ya ce, wanda ake zargin ya na hannun su tare da ci gaba da gudanar da bincike a kan shi.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp