fidelitybank

Matashin da ya shiga aikin DSS da takardar jabu ya rataye kansa a Kano

Date:

Wani matashi mai kimanin shekaru 29 mai suna, Bashir Ibrahim, ya hallaka kansa har lahira ta hanyar rataye kansa a unguwar Hagagawa dake karamar hukumar Bichi a jihar Kano.

Kadaura24 ta rawaito matashin a na hasashen ya kashe kansa ne saboda karar shi daga aiki da hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta yi, sakamakon samun sa da akai da shaida karatun NCE ta Jabu.
” Da ma ya shiga aikin ne na DSS da takardar NCE ta Jabu, su Kuma suka yi bincike har suka gano shi , to shi ne fa suka kore shi daga aiki” . Inji Majiyar Kadaura24
Lokacin da kadaura24 ta zanta da wani dan uwan mamacin wanda ya bukaci a sakaye sunansa yace tun lokacin da aka sallami mamacin daga aiki ya shiga damu wanda suna zaton hakan ne yasa Bashir ya rataye kansa.
” Duk da yake bai fadawa kowa cewa zai kashe kansa ko dalilin da yasa ya hallaka kansa ba, sannan kuma bai ajiye wata alama ko dalilin da yasa ya aika hakan ba , Amma dai muna ganin yayi hakan ne sakamakon korar sa da akai daga aiki da kusan  makwanni uku da suka gabata”.
Dan Uwan mamacin ya ce tuni dai akai jana’izar mamacin kamar yadda addinin musulunci ya tanada da misalin karfe 9 na daren jiya Alhamis a garin Bichi dake jihar kano.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp