Wani matashi mai kimanin shekaru 29 mai suna, Bashir Ibrahim, ya hallaka kansa har lahira ta hanyar rataye kansa a unguwar Hagagawa dake karamar hukumar Bichi a jihar Kano.
Kadaura24 ta rawaito matashin a na hasashen ya kashe kansa ne saboda karar shi daga aiki da hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta yi, sakamakon samun sa da akai da shaida karatun NCE ta Jabu.
” Da ma ya shiga aikin ne na DSS da takardar NCE ta Jabu, su Kuma suka yi bincike har suka gano shi , to shi ne fa suka kore shi daga aiki” . Inji Majiyar Kadaura24
Lokacin da kadaura24 ta zanta da wani dan uwan mamacin wanda ya bukaci a sakaye sunansa yace tun lokacin da aka sallami mamacin daga aiki ya shiga damu wanda suna zaton hakan ne yasa Bashir ya rataye kansa.
” Duk da yake bai fadawa kowa cewa zai kashe kansa ko dalilin da yasa ya hallaka kansa ba, sannan kuma bai ajiye wata alama ko dalilin da yasa ya aika hakan ba , Amma dai muna ganin yayi hakan ne sakamakon korar sa da akai daga aiki da kusan makwanni uku da suka gabata”.
Dan Uwan mamacin ya ce tuni dai akai jana’izar mamacin kamar yadda addinin musulunci ya tanada da misalin karfe 9 na daren jiya Alhamis a garin Bichi dake jihar kano.