fidelitybank

Matashin da ya kwakulewa yaro ido a Kano ya shiga hannu

Date:

Rundunar ƴan sandan Kano ta tabbatar da kama wata tsohuwa da ake zargin ta saka wani matashi mai shekara 17 ya ƙwaƙulewa wani yaro mai suna Mustapha Dahiru ido don a haɗa musu layar zana.

Rundunar ƴan sanda ta ce ta kamo matar ne bayan koke da suka samu daga jama’ar unguwa da ƴan sa kai na yankin unguwar Dan Tsinke a karamar hukumar Tarauni a Kano.

Tun kafin ƴan sanda su kai ga kamo matar da ake zargi da sa matashin ya cirewa yaron ido, kungiyar tsaro ta ‘yan sa-kai ta Dan Tsinke da ke kusa da Unguwar Sheka suka kamo matashin da ake zargi da cirewa yaron ido ɗan shekaru 10-11.

Matashin da ake zargi ya shaida musu cewar wata tsohuwa ce ta umarci da ya kawo mata ido don ta hada masa layar zana, kamar yadda Rabi’u Suleiman Mai Matasa mataimakin sakatare na kungiyar ‘yan-sa kai ta Dan Tsinke a Kano ya shaidawa BBC.

SP Abdullahi Kiyawa kakakin ƴan sanda a Kano ya tabbatar da faruwar al’amarin, ya kuma ja hankulan al’umma da su ringa sanya ido kan abubuwan da ke faruwa a kewayen su, don kaucewa afkuwar irin wannan lamari.

Ko a makon da ya gabata sai da aka sami waji matashi da ya tura ‘yar uwarsa a cikin rijiya, a yankin karamar hukumar Rimin Gado a Kano, tare da wani matashi da ya kashe wata yarinya, yar makwabcin gidansu, bayan da ya nemi kudin fansa.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp