Rundunar ƴan sandan Najeriya reshen Jihar Kano ta kama wani matashi ɗan shekara 18 bisa zarginsa da kashe matar aure a Jihar.
A wata sanarwa da mai magana da yawun yan sanda reshen Jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, lamarin ya faru ne a Karamar Hukumar Kumbotso.
Wanda ake zargi da aikata kisan mai suna Abdulsamad Suleiman, ya amsa laifin ga ƴan sandan inda ya ce tun da farko ya shiga gidan matar inda ya same ta a kan gado, bayan ya gaishe ta sai ya ga wayoyi uku sa’annan ya sace su, in ji kakakin ‘yan sndan.
SP Kiyawa ya kara da cewa, bayan matashin ya gano cewa matar ta gane shi, sai ya yi amfani da taɓarya ya yi ta buga mata a kai, haka kuma ya buga wa ƴaƴanta biyu taɓaryar sa’annan ya gudu da wayoyin.