Rundunar ƴansandan jihar Kano ta ce ta kama wani matashi bisa zargin kashe saurayin ƙanwarsa a lokacin da ya je zance gidansa.
Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar ya ce lamarin ya faru ne a ƙauyen Kunya da ke yankin ƙaramar hukumar Minjibir.
Sanarwar yansandan ta ce matashin wanda ɗan asalin ƙauyen Goda, ya je Kunya ne wajen budurwarsa domin zance, sai dai jim kaɗan bayan zuwan nasa sai aka yi zargin cewa yayan budurwar mai suna Mansur Umar mai shekara 25 ya doke shi da sanda a ka, lamarin da ya haddasa masa munanan raunuka.
”Tuni aka garzaya da shi asibitin Kunya daga baya kuma aka mayar da shi asibitin Murtala domin ba shi kulawar gaggawa, inda daga baya aka tabbatar da mutuwarsa”, a cewar ƴansandan.
Ƴansanda sun ce tuni suka kama Mansur, domin gudanar da bincike a sashen binciken manyan laifuka na rundunar ƴansandan jihar.
Rundunar ƴansandan ta yi kira ga jama’a su riƙa sanya haƙuri a cikin al’amuransu, tare da kai rahoton duk wata jayayya da aka samu tsakanin wasu mutane zuwa ofishin ƴansanda mafi kusa.