Rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, ta cafke wani mutum mai suna Dauda Bello mai shekaru 34 da haihuwa da laifin kashe wata mata mai suna Mesesi Adisa ‘yar shekaru 71 da haihuwa tare da sayar da hannunta da idonta ga wani da ake zargi da aikata tsafi.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Abimbola Oyeyemi, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.
Oyeyemi ya ce, an kama wanda ake zargin ne a ranar Alhamis bayan wanda aka kashe ya bar gida ba zato ba tsammani a ranar 8 ga watan Yuni 2022.
Yayin da ake binciken bacewar tsohuwar matar, jami’an tsaro sun gano ta zuwa inda aka ganta na karshe wato gidan wanda ake zargin.
Ya ce: “Daga baya an mayar da shari’ar zuwa sashin yaki da garkuwa da mutane na sashen binciken manyan laifuka na jihar inda aka fara gudanar da bincike na fasaha da na sirri.
“A yayin gudanar da bincike, rundunar ‘yan sandan ta SP Taiwo Opadiran, ta gano wuri na karshe da wanda abin ya shafa ya ziyarta a unguwar Olodo da ke Imala.