fidelitybank

Matashi ya sha kwaya ya mutu a ranar murnar haihuwarsa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas, ta tabbatar da mutuwar wani matashi mai shekaru 21 mai suna Micheal Arigbabuwo, wanda ya rasa ransa a wajen bikin zagayowar ranar haihuwarsa, bayan da aka zarge shi da hada wasu kwayoyi masu tsauri guda biyu don yin tasiri.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda (PPRO) a jihar Legas, SP Benjamin Hundeyin ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter.

Hundeyin wanda ya tabbatar da kame uku daga cikin abokan mamacin ya ce, lamarin ya faru ne a ranar Juma’a a unguwar Ikorodu da ke jihar Legas.

Ya ce bayanan da ‘yan sanda suka samu a Ikorodu sun nuna cewa da misalin karfe 7:30 na yammacin ranar Juma’a ne, aka yi kira da nuna damuwa cewa wasu ‘yan kungiyar Yahoo Yahoo sun kawo gawa zuwa yankin Igbogbo da ke Ikorodu.

“Bisa bayanin, gungun masu binciken sun ziyarci inda lamarin ya faru kuma suka dauki hoto. An kama wasu matasa uku masu shekaru 23 da 24.

“Wadanda ake zargin sun yi ikirarin cewa marigayin ya sha hayaki da karfi kuma ya sha codeine a wajen bikin zagayowar ranar haihuwar daya daga cikin abokansu da aka gudanar a yankin Igbogbo a Ikorodu.

“Wadanda ake zargin sun kara da cewa marigayin ya fara haki. An garzaya da shi asibiti amma ya mutu,” inji shi.

Hundeyin ya kara da cewa an kwashe gawar an ajiye ta a babban asibitin Ikorodu domin a tantance gawar.

Don haka ya gargadi matasa kan shaye-shayen miyagun kwayoyi, yana mai jaddada cewa, miyagun kwayoyi za su kawo karshen rayuwarsu cikin bala’i.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp