Wani matashi mai suna Kido ya kashe mahaifinsa a gonar su, bayan sun yi taho-mu-gama da shi bisa zarginsa na girbin amfanin gona ba tare da izinin mahaifinsa ba a unguwar Issele-Uku da ke jihar Delta.
Jama’ar Ukpai ne suka kama wanda ake zargin kuma DAILY POST na iya bayar da rahoton cewa ya yi ikirari.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Delta, DSP Bright Edafe ne ya tabbatar da hakan a wani sako da ya aike ta WhatsApp.