An kama wani da ake zargi maia suna, Ogaga Kome, da laifin kashe wani matashi mai suna Hossanna Merritt mai shekaru 11, a lokacin da yake gwada wata bindigar gida a gidansa.
Lamarin ya faru ne a unguwar Ozoro da ke yankin karamar hukumar Isoko ta Arewa a jihar Delta a ranar Litinin din da ta gabata.
Rahotanni sun bayyana cewa wanda ake zargin mai shekaru 26 ya gudu bayan faruwar lamarin.
“Saboda haka, a ranar 30/8/2022 da misalin karfe 1305, wani mutum mai kishi wanda kuma dan uwan wanda ake zargin ne ya kawo shi ofishin. Wanda ake zargin yana tsare kuma ana ci gaba da gudanar da bincike,” in ji jami’an tsaro.