fidelitybank

Matasan Zamfara ku guji siyasar kuɗi – Abubakar

Date:

Wani mai sharhi kan al’amuran siyasa a Zamfara, Abubakar Abdulkarim, ya shawarci mazauna yankin musamman matasa da su guji siyasar kudi, domin tabbatar da samar da ababen more rayuwa da ci gaban jihar baki daya.

Abdulkarim ya koka da yadda siyasar kudi ta kwace ‘yancin jama’a na yin tambaya game da almundahana da shugabannin su ke yi, jinkirin albashi, almubazzaranci da dukiyar al’umma, rashin kudi, tara basussuka da dai sauransu.

Da yake zantawa da jaridar DAILY POST a Gusau, babban birnin jihar, Abdulkarim ya ce akwai bukatar jama’a su koma kan hukumar zana da nufin samar da ingantattun tsare-tsare na siyasa da za su magance munanan halin da jihar ke ciki.

Ya ci gaba da cewa, ya kamata a yi taka-tsan-tsan bisa la’akari da matsalolin da suka dabaibaye jihar baki daya, yana mai cewa dole ne a guji siyasar kudi idan har jama’a na son fitar da kansu daga cikin wadannan matsaloli.

Abdulkarim ya yi gargadin cewa kada siyasar Zamfara ta zama sana’a kamar yadda aka saba biyo bayan kalubale da dama da ke fuskantar mazauna yankin, inda ya nuna cewa dole ne su yi amfani da kuri’unsu yadda ya kamata domin gujewa ‘da mun sani’.

“Suna bukatar baiwa wani mutum da ke da niyyar siyasa wanda zai iya kare su daga halin rashin tsaro da ke addabar jihar, ya ciyar da ‘yancinsu na tattalin arziki, samar da kudaden shiga na yau da kullun, ingantaccen rayuwa.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp