fidelitybank

Matasan da suka fusata sun sa an goge shafin Facebook na Rarara a kan waƙar Tinubu

Date:

Bayanai na cewa an goge shafin fitaccen mawaƙin siyasar nan Dauda Kahutu Rarara daga dandalin Facebook

Hakan na zuwa ne bayan da aka yi zargin cewa wasu masu amfani da dandalin ne suka riƙa kai ƙorafin shafin nasa ga kamfanin na Facebook,(reporting) bayan ya wallafa wata sabuwar waƙa a shafin nasa da ake zargin ba ta yi wa matasan daɗi ba.

A ‘yan kwanakin nan ne dai mawakin ya fitar da wata sabuwar waƙa da ya wallafa a shafukansa na sada zumunta.

Waƙar dai ta ƙunshi yabo ga shugaban Najeriya, Bola Tinubu kan wasu ayyukan da mawaƙin ke iƙirarin shugaban ya samar wa ƙasar.

An ji yo Rarara cikin wasu baitocin wakar na cewa:

“Tinumbu ya gama mana aiki ba batun ɓoyo,

”yanzu talauci ƙyaram, yunwa ƙyaram,

”kana security daram-dam-dam, ƴanci daram,

”Sannu farin cikin ƙasa Tinubu, sai godiya, baba makaniken gyara lamba ɗaya”.

Sabuwar waƙar na zuwa ne a daidai lokacin da wasu matasan ƙasar ke shirin gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwa da yunwa da rashin tsaro da ƙasar ke fama da su.

Wannan dalilin ne ya sa suke kallon waƙar tamkar izgili ko zolaya mawaƙin ke yi wa ‘yan ƙasar, lamarin da ya sa suka ɗauki matakin gangamin kai ƙorafin shafin nasa zuwa ga kamfanin Facebook, domin buƙatar kamfanin ya goge shafin.

Bayan kamar kwana biyu da fara gangamin, Facebook ya goge shafin – mai mabiya fiye da miliyan guda daga dandalin. In ji BBC.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp