Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta kama wasu matasa uku da suka addabi mazauna garin Aujarawa Alkali da ke karamar hukumar Gezawa da sata.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce, binciken ya kai ga cafke wanda ya sayi dabbobin da aka sace.
A halin da ake ciki, Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasa ya kuma ruwaito cewa, wani mutum mai shekaru 51, Ademola Adetoun, a ranar Litinin, ya gurfana a gaban wata kotun majistare da ke Ikorodu a jihar Legas bisa laifin satar awaki hudu.
Dan sanda mai shigar da kara, Sefata Christian Okonofua, ya shaida wa kotun cewa, wanda ake tuhumar ya aikata laifin ne a wani lokaci a watan Janairu, a lamba 1, Living Fountain, Owode Elede da ke kan titin Ikorodu a Ikorodu.