fidelitybank

Matasa sun yi zanga-zanga a tsige kwamishinan zabe na Akwa Ibom

Date:

Wasu fusatattun matasa a karkashin gamayyar jam’iyyun siyasa a ranar Laraba sun tare ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a jihar Akwa Ibom.

Matasan wadanda akasari ‘ya’yan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ne suka bukaci da a gaggauta tsige kwamishinan zabe na mazaunin yankin Mista Mike Igini.

Masu zanga-zangar da yawansu ya haura 1000 sun zargi Igini da karkata daga matsayinsa na alkali marar son rai zuwa wani dan siyasa mai son kawo rudani a jam’iyyar APC reshen jihar.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa masu zanga-zangar da suka yi wa Mike Igini ya tafi, sun tare kofar ofishin INEC inda suka hana ma’aikatan Hukumar shiga ofisoshinsu.

An gan su dauke da alluna dauke da rubuce-rubuce daban-daban da ke cewa; “Igini son zuciya”, “Dimokradiyya ba siyarwa bane”, “Dole ne INEC ta yi aiki a yanzu”, “Akwa Ibom REC is compromised”.

Sauran su ne; “Igini ba sa kashe jam’iyyun siyasar Akwa Ibom”, “Igini dan jam’iyya ne”, “Igini shugaban jam’iyya ne na bangare”, da dai sauransu.

“Wannan zanga-zangar dukkan matasa ne a jam’iyyun adawa a jihar Akwa Ibom kuma jam’iyyar APC duk ta shahara a nan domin ita ce babbar jam’iyyar adawa a jihar.

“Muna zanga-zangar nuna rashin amincewa da nuna bangaranci da wani da ake zaton alkali ne, Kwamishinan Zabe, Barr. Mike Igini.

www.legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp