fidelitybank

Matasa sun kashe wanda ya yi kalaman batanci a Bauchi

Date:

Gungun wasu matasa ya kashe wani mutum mai suna Yunusa bisa zargin yin kalamai na ɓatanci ga Annabi Muhammadu (SAW), a ƙaramin ofishin ƴansanda na Nasaru da ke ƙaramar hukumar Ningi a jihar Bauchi.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3 na rana, shekaran jiya Laraba, lokacin da musu ya ɓarke tsakanin shi Yunussan da kuma wani mutum, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Wani da aka yi abin a gaban idonsa, wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya yi bayanin yadda da farko ƴansanda suka ceci Yunusan lokacin da jama’a suka fara dukan mutumin.

Ya ce, ”ƴansanda sun kai mutumin da ake zargin ƙaramin ofishinsu a cikin garin, amma kuma mutanen sun ci ƙarfinsu, inda suka kashe shi.”

Mutumin ya ƙara bayani da cewa bayan sun kashe Yunusan ne ƙaramin ofishin na Nasaru, sai suka ɗauki gawarsa suka kai ofishin ƴansanda na Ningi.

Rundunar ƴansanda ta jihar Bauchi ta tabbatar da faruwar lamarin.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp