A ranar Laraba ne wasu guggun matasa su sama da 30 dauke da duwatsu da katako da sauran muggan makamai, sun kai hari a ofishin hukumar babban birnin tarayya Abuja a unguwar Kuchingoro da ke Abuja.
Jami’an rundunar biyar sun samu raunuka daban-daban yayin da aka mika wadanda ake zargi 10 ga ‘yan sanda, domin bincike da gurfanar da su gaban kuliya.
Hukumar ta ci gaba da aiwatar da gagarumin aikin tsare wuraren tare da damke masu tuka babura na kasuwanci da suka saba ka’idojin zirga-zirga da rushe wuraren da basu dace ba a hanyar Lugbe zuwa tashar jirgin sama.
Babban mataimaki na musamman (SSA) akan sa ido, dubawa da aiwatarwa ga Ministan babban birnin tarayya, Ikharo Attah, wanda ya na cikin jami’an da suka tsira da ransu, ya ce ‘yan ta’addan sun fusata a lokacin da suke aiwatar da ayyukan su.