fidelitybank

Matasa ku kauce wa hargitsi lokacin zanga-zanga – Gwamnan Osun

Date:

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya gargaɗi ƴan ƙungiyoyin fararen hula da al’ummar jihar su kauce wa hargitsi a lokacin zanga-zanga da ake shirin gudanarwa daga ɗaya zuwa 10 ga watan Agusta a jihar.

Gwamna Adeleke, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Prince Kola Adewusi tare da wasu ‘yan majalisar zartarwa na jihar Osun ya bayar da shawarar ne a wata tattaunawa da mambobin ƙungiyoyin farar hula na jihar a yau Talata.

Gwamnan ya ce duk da cewa ya san ƴan kasa na da ƴancin yin zanga-zanga, su tabbatar da cewa ba su saka rayuwar ƴan jihar cikin haɗari ba.

Gwamnan ya ce “kwanciyar hankali da lafiyar ƴan jihar Osun shi ne babban damuwarmu da abin da muka fi mayar da hankali a kai a zanga-zangar da ake shirin gudanarwa.”

“Babban burina a matsayin gwamnan wannan jihar shi ne mayar da jihar a matsayin babban misali mai kyau ga sauran jihohi,” in ji gwamnan.

“Saboda haka ne na shawarce ku ƴan jihar Osun da ku kasance masu biyaya ga doka da oda a lokacin zanga-zanga da kuma bayan zanga-zanagar, ba za mu amince da duk wani hargitsi ba da tashin hankali yayin da kuke gudanar da zanga-zanga.” in ji gwamnan.

Ƙungiyoyin fararen hula da sauran ƙungiyoyi masu zaman kansu na jihar sun yaba wa gwamnan da gudanar da irin wannan tattaunawar inda suka ce sun amince za su yi biyayya ga doka da kuma tabbatar da an yi zanga-zangar cikin lumana.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp