fidelitybank

Matasa ku guji shiga bangar siyasa a zaben 2023 – Sarkin Kano

Date:

Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya shawarci matasa da su guji shiga banga a zabe mai zuwa yayin da aka fara yakin neman zabe.

Sarkin ya ba da wannan shawarar ne a ranar Asabar a lokacin da ya jagoranci taron addu’o’i ga kasar a wani bangare na ayyukan da Masarautar ta shirya domin tunawa da cikar kasar shekaru 62 da samun ‘yancin kai.

Ya kuma gargade su (matasa) da ka da su bari ‘yan siyasa su yi amfani da su wajen biyan bukatunsu na son kai, inda ya bukace su da su guji aikata ayyukan da za su iya haifar da tashin hankali a jihar musamman ma kasa baki daya.

“Ina so in yi amfani da wannan damar domin yin kira ga matasa da su guji ‘yan daba su guje wa ayyukan da za su iya haifar da tashin hankali a lokacin zabe,” in ji Sarkin.

Sarkin ya kuma yi kira ga ‘yan siyasa a kasar da su daina yin kalamai marasa gadi da kalaman nuna kiyayya a lokacin yakin neman zabe.

Ya ce an yanke shawarar shirya tarukan addu’o’in ne da nufin neman taimakon Allah don ganin an gudanar da zabe cikin lumana a kasar nan a 2023.

“An shirya taron addu’o’in ne domin yi wa kasa addu’a a daidai lokacin da ake bikin cika shekaru 62 da samun ‘yancin kai domin ganin an gudanar da zaben 2023 cikin nasara,” inji Bayero.

Sarkin ya bayyana fatan ’yan siyasa za su yi amfani da shawarar da dattawa da malamai daban-daban suke ba su wajen gujewa duk wani abu da zai zafafa harkokin siyasa.

Taron addu’ar ya samu halartar ‘yan majalisar Masarautar da kuma sauran masu hannu da shuni daga sassa daban-daban na jihar.

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...
X whatsapp