Hukumar kashe gobara ta jihar Kano, ta tabbatar da rasuwar wasu matasa biyar, yayin da suke hakar kasa a kauyen Yan Lami a karamar hukumar Bichi.
Dailytrust ta rawaito cewa, da ya ke tabbatar da afkuwar lamarin, mai magana da yawun hukumar, Saminu Yusuf Abdullahi, ya ce matasan sun rasa ransu ne yayin da suke hako kasa da za a yi amfani da ita a wurin gina wa abokinsu wanda zai yi aure gida.
“Lokacin da mutanen mu suka isa wurin da abin ya faru, matasan biyar sun riga sun rasu a wurin da suke hako kasar. “Mutanen sun hada da Alasan Abdulhamid mai shekara 22, Muhammad Sulaiman mai shekaru 35; Dauda Nasir dan shekara 25; Jibrin Musa dan shekara 30 da Ja’afaru Abdulwahabu shima dan shekara 30,” in ji Saminu.
Ya kara da cewa hukumar ta mika gawarwakin matasan da abin ya faru da su ga hakimin Yan Lami domin a musu jana’iza bisa koyarwar addinin musulunci.