An kashe mutane biyu a lokacin da wasu ‘yan bindiga suka yi wa ayarin motocin zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Jos ta Arewa/Bassa, Musa Agah kwantan bauna a daren ranar Talata.
Rahotanni na nuni da cewa, dan majalisar yana dawowa ne daga Jebbu Bassa bayan ya zagaya unguwanni hudu na masarautar Rukuba na karamar hukumar Bassa.
Mataimakin dan majalisar, Moses Maly, wanda ke cikin mota daya tare da shi a lokacin da lamarin ya faru, ya bayyana cewa matar dan majalisar da ‘ya’yansa biyu su ma suna tare da shi, amma duk sun tsere yayin da motar sa harsashen alburushi suka farfasa ta.
Maly ta kara da cewa an kashe mutane biyu da ke kan babur da suka hada da shugaban gundumar PDP da shugabar mata da ke gaban ayarin motocin.
Kwanan nan ne aka rantsar da dan majalisar, a matsayin dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Jos ta Arewa/Bassa bayan nasarar da ya samu a zaben fidda gwani na ranar 26 ga Fabrairu, 2022.