fidelitybank

Matar da ta jefa jaririyar ta cikin teku ta shiga hannu

Date:

‘Yan sandan Kenya sun kama wata mata da ake zargi da jefa jaririyarta ƴar watanni takwas a cikin tekun Indiya ranar Lahadi.

Shaidu sun shaida wa kafafen yaɗa labaran kasar cewa, matar ta jefa jaririyar ne cikin teku daga wani jirgin ruwa a lokacin da ya doshi garin Mombasa da ke gaɓar teku.

Bidiyon yadda ake ceto jaririyar ya karaɗe shafukan sada zumunta, lamarin da ya sa al’ummar Kenya da dama ke nuna ɓacin ransu ga matar da kuma jin dadin yadda aka ceto jinjirar.

“An garzaya da jaririyar don ba da agajin farko a cibiyar agaji ta Red Cross, inda aka kula da ita sannan aka sallame ta cikin yanayi mai kyau, an kuma kai mahaifiyarta ofishin ‘yan sanda domin yi mata tambayoyi.” kamar yadda kafafen yaɗa laarai na K24 da Citizen TV suka ruaito.

Tun farko ƙungiyar agaji ta Red Cross ta Kenya ta ce jariririyar tana cikin ƙoshin lafiya a cibiyarta ta agaji.

Har yanzu dai ba a bayyana ko irin tuhume-tuhumen da za a yi wa matar ba. In ji BBC.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp