A na zargin wata mata da yunkurin yin garkuwa da wani dalibi mai shekaru 5 Bashir Jamilu, a Jihar Kano.
Bashir Jamilu dan makarantar firamare ta Ulumuddin da ke Koki, kuma an yi zargin yunkurin sace shi da misalin karfe 8:30 na safiyar Talata, lamarin ya faru ne a kan hanyar zuwa makarantar ne matar ta rike hannunsa ta na ce masa za ta sai masa nama da madara amma sai ya fara kuka.
Dailytrust ta rawaito cewa, Mahaifiyar dalibin, Aisha Salisu Koki ta sanar da cewa ta tura shi makaranta da misalin karfe 8:30 na safiyar Talata amma a hanyarsa wata mata ta rike hannunsa ta ce za ta siya masa nama, indomi da madara, sai yaron ya ki yarda ya fashe da kuka.
A bangaren Nasiru Ayuba Yusuf, kwamandan rundunar ‘Yan Sa Kai na Koki, ya ce, a lokacin da matar take jan yaron ‘Yan Sa Kan da suka gan ta sun yi zaton mahaifiyarsa ce zata kai shi makaranta tunda sanye yake da kayan makaranta.