fidelitybank

Matar da aka samu da laifin bin Maza kotu ta ce a kashe ta a Iran

Date:

Kafofin yaɗa labarai a Iran sun ruwaito cewa kotu a birnin Tehran ta yanke wa wata mata hukuncin kisa bayan kama ta da laifin “cin amanar mijinta.”

Bayanai sun ce mutumin mai suna Parham ya gano cewa matar tasa tana hulɗa da wasu maza ne bayan ya sanya kyamarar tsaro ta CCTV a gidansa.

Ma’auratan biyu sun kwashe shekara 10 a tare.

Mutumin ya ce bayan sanya kyamarori a gidansa sai ya rinƙa ganin wasu maza suna shige da fice a gidan a lokacin da ba shi nan.

A lokacin da aka tuhume ta, matar ta ce ta shiga halin neman maza ne saboda “kaɗaici”, kuma bayanai sun nuna cewa takan gabatar da kanta ga mutane a matsayin mai horas da wasannin motsa jiki.

Ɗaya daga cikin mazan da ta nema ya bayyana cewa “bai ga wata alama da ta nuna cewa matar tana da aure ba.” Kotun ta yanke wa mutumin hukuncin bulala.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp