Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Adamawa, ta kama wata matar aure ‘yar shekara 20, Caroline Barka, bisa zargin kashe mijinta, Dauda Barka.
Rahotanni sun bayyana cewa, Barka ta daba wa mijinta wuka ne a lokacin da suke fafata rikici, wanda ya yi sanadiyyar mutuwarsa, kamar yadda rahoton ‘yan sanda ya bayyana.
SaharaReporters ta samu labarin cewa, Barka, ta kashe mijinta mai shekaru 38 da haihuwa, saboda ya rika shaye-shaye cikin dare, da dai sauran batutuwan da suka tayar da hankali.
Kamar yadda muka tattaro, lamarin ya faru ne a ranar Juma’a a Anguwan Tsamiya da ke karamar hukumar Madagali a jihar.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa, SP Suleiman Nguroje, ya ce: “Rikici ya barke tsakanin ma’auratan bayan mijin ya dawo gida a makare ya bugu.
“Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa a ranar 22/7/2022 ta kama wata matar aure ‘yar shekara 20, bisa laifin kashe mijinta mai shekaru 38 da haihuwa.
“Bincike ya zuwa yanzu ya nuna cewa, wanda ake zargin kasancewarta mai shayarwa tana tare da marigayiyar bayan shekaru biyu da aure,” inji shi.