fidelitybank

Matan jam’iyyar APC ba abun yarwa ba ne – Gawuna

Date:

Mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya yabawa matan jam’iyyar APC, bisa gudunmawar da suke bayarwa wajen ci gaban jihar.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugabar mata ta jam’iyyar APC ta jihar kano, Hajiya Fatima Abdullahi Dala, wadda ta jagoranci tawagar shugabannin mata da sauran jiga-jigan jam’iyyar a fadin kananan hukumomi 44 da suka kai masa ziyarar taya murna kan lashe zaben fidda gwani na dan takarar Gwamnan kano a jam’iyyar APC.

Cikin Sanarwar da babban Sakataren yada labaran Mataimakin Gwamna Hassan Musa fagge ya aikawa manema labarai, ya ce, ya yi imanin matan da aka san su da aminci, sadaukarwa da jajircewa za su marawa APC baya wajen samun nasara a lokacin babban zabukan shekara ta 2023.

Mataimakin Gwamnan ya umarce su a matsayinsu na Iyaye kuma masu son ci gaba da su ci gaba da koyar da kyawawan dabi’u ga yara ta hanyar basu tarbiyya domin samun al’umma ta gari.

Gawuna ya kuma bayyana cewa an baiwa mata a Kano damammaki Masu yawa saboda gwamnatin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje tana sane da irin rawar da suke takawa, iya karfinsu, wajen samun nasara a zabukan da Suka gabata.

Ya kuma gode musu bisa ziyarar tare da bada tabbacin ci gaba da ba su goyon baya domin samun nasarar jam’iyyar APC. In ji Kadaura.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp