fidelitybank

Matan jam’iyyar APC ba abun yarwa ba ne – Gawuna

Date:

Mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya yabawa matan jam’iyyar APC, bisa gudunmawar da suke bayarwa wajen ci gaban jihar.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugabar mata ta jam’iyyar APC ta jihar kano, Hajiya Fatima Abdullahi Dala, wadda ta jagoranci tawagar shugabannin mata da sauran jiga-jigan jam’iyyar a fadin kananan hukumomi 44 da suka kai masa ziyarar taya murna kan lashe zaben fidda gwani na dan takarar Gwamnan kano a jam’iyyar APC.

Cikin Sanarwar da babban Sakataren yada labaran Mataimakin Gwamna Hassan Musa fagge ya aikawa manema labarai, ya ce, ya yi imanin matan da aka san su da aminci, sadaukarwa da jajircewa za su marawa APC baya wajen samun nasara a lokacin babban zabukan shekara ta 2023.

Mataimakin Gwamnan ya umarce su a matsayinsu na Iyaye kuma masu son ci gaba da su ci gaba da koyar da kyawawan dabi’u ga yara ta hanyar basu tarbiyya domin samun al’umma ta gari.

Gawuna ya kuma bayyana cewa an baiwa mata a Kano damammaki Masu yawa saboda gwamnatin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje tana sane da irin rawar da suke takawa, iya karfinsu, wajen samun nasara a zabukan da Suka gabata.

Ya kuma gode musu bisa ziyarar tare da bada tabbacin ci gaba da ba su goyon baya domin samun nasarar jam’iyyar APC. In ji Kadaura.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp