Tsohon shugaban mulkin soja na farko a jihar Abia kuma jigo a jam’iyyar APC a jihar Delta, Air Vice Marshal Frank Ajobena ami ritaya ya fice daga jam’iyyar.
Ajobena ya fice daga APC ne saboda shawarar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Bola Tinubu, ya yanke na neman tikitin takarar Musulmi da Musulmi.
Dan jam’iyyar APC na kasa ya ce tikitin takarar Musulmi da Musulmi na jam’iyyar shi ne “mafi girman matakin rashin kishin addinin Kirista a kasar nan.”
A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, Ajobena ya ce Tinubu bai mutunta kiristoci a kasar nan ba.
Ya jaddada cewa ,matakin da Tinubu ya dauka ya nuna cewa ‘yan jam’iyyar APC za a iya saye su da kudi cikin sauki.