Shugaban kasa Bola Tinubu ya nanata kira ga ƴan Najeriya da su ƙara haƙuri domin akwai haske a gaba, sannan ya ƙara da cewa gwamnatinsa mai sauraron koken jama’a ce.
Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Juma’a, lokacin da ya karɓi baƙuncin ƙungiyar fastocin Cocin Katolika ta Catholic Bishop’s Conference of Nigeria (CBCN) a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.
Ya bayyana wa malaman cocin cewa ya ɗauki matakai masu tsauri bayan ya karɓi mulki a shekarar 2023, ciki har da cire tallafin man fetur.
“Lallai cire tallafin man fetur mataki ne mai tsauri, amma ya zama dole ne domin ba za mu cigaba da jinginar da ƙasarmu ba,” in ji shi, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito daga mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga.
“Sai dai akwai alamun nasara da sauƙi a gaba. Ana bayyana abubuwa masu kyau game da Najeriya, kuma ina alfahari da haka. Matakan masu tsauri yanzu sun fara nuna alamomi masu kyau.”
Ya ce damina ta yi albarka wanda hakan ya sa farashin kayan abinci yake sauka, sannan farashin man fetur ma yana sauka.
A game da batun hare-haren ta’addanci, Tinubu ya ce rashin tsaro yana shafar musulmi da kirista, inda ya ƙara da cewa matarsa kirista ce, don haka ba zai zama mai yi musu kisan mummuƙe ba.