fidelitybank

Matakai mai tsauri mu ke ɗauka don mu gina Najeriya – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya ce, gwamnatinsa na ɗaukar matakai masu tsauri ne domin gina ƙasar tare da samar mata ingantaccen ci gaba.

Yayin da yake jawabi ga ƙungiyar ‘yan asalin Najeriya mazauna China, a birnin Beijing, Shugaba Tinubu ya ce an ƙara farashin man fetur ne a ƙasar, domin samar wa Najeriya ingantaccen ci gaba.

”Za ku ji a ‘yan kwanakin nan ana ta magana game da ƙarin kuɗin man fetur, amma magana ta gaskiya za mu iya gina ƙasarmu? Mu samu tituna masu kyau kamar yadda muka gani a nan (China), mu samu tsayayyiyar wutar lantarki da ruwan sha, kuma kun dai ga yadda makarantunsu ke da kyau a nan”, in ji Tinubu.

Ya ƙara da cewa ”idan muna son cimma waɗannan abubuwa sai mun ɗauki matakai masu tsauri domin samun hanyar da za ta kai mu ga ciyar da ƙasarmu gaba”.

Shugaban ƙasar ya ce ba a samun kowane irin ci gaba cikin sauƙi ko kuma a ɓagas.

“Idan kana son ka samu komai a kyauta, to zai zame maka mai wahalar samu ko ka jima ba ka same shi ba”, in ji shugaban na Najeriya.

”Kalli tituna masu kyau da inganci a nan, ina so na kwaikwayi irin waɗannan ayyuka a Najeriya, ina son gyara makarantun ‘ya’yanmu, bana son ganin ɗalibanmu suna zama a azuzuwan da suka lalace, ina son gayar tsarin koyarwa”, in ji shi.

A ranar Talata ne dai babban kamfanin mai na asar NNPCL ya sanar da ƙarin kuɗin man fetur zuwa naira 855, dangane da inda mutum ke zaune a ƙasar, lamarin da ya ya janyo wa gwamnatin ƙasar suka daga ƙungiyoyi da ɗaiɗaikun mutane.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp