fidelitybank

Mataimakin shugaban majalisar dattawa ya ayyana takarar kujerar gwamna a Delta

Date:

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Obarisi Ovie Omo-Agege,  ya bayyana cewa, zai tsaya takarar gwamnan jihar Delta a karkashin jam’iyyar APC.

Kafin ya ayyana shiga takarar gwamna, Omo-Agege ya nemi afuwar magoya bayansa sama da dubu goma da suka isa filin wasan kwallon kafa na jami’ar tarayya ta albarkatun man fetur da ke Effurun da misalin karfe 7 na safe, amma an fara shirin ne da misalin karfe hudu na yamma.

Ya ce, duk da zuwa da wuri da magoya bayan, sun ci gaba da hakuri abin da ya ce, alama ce ta APC a shirye take ta fatattaki PDP daga jihar.

Omo-Agege ya ce, zai kawo sauyi a jihar Delta nan da kasa da shekaru hudu, yana mai cewa, ko a matsayinsa sa na Sanata ya yi ayyuka da dama a mazabar sa kuma idan aka zabe shi gwamna zai tabbatar da cewa, an samu ci gaba a gundumomin Sanata uku.

Ya ce, duk alkawurran da ya dauka yayin da ya bayyana tsayawa takarar majalisar dattawa ya cika su.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp