Kelvin Ejeh ya yi murabus daga mukaminsa na mataimakin kocin kungiyar kwallon kafa ta Najeriya, Abia Warriors.
Ejeh, wanda ya shafe sama da shekaru goma yana tare da Ochendo Boys, ya yi murabus daga mukaminsa a ranar Juma’a.
Ya kasance mai horar da matasan kungiyar Abia Warriors a shekarar 2015 kafin daga bisani a kara masa girma zuwa tawagar farko.
Ejeh ya bayyana cewa murabus din nasa zai bashi damar lalubo wasu hanyoyin da zai bi wajen gudanar da aikinsa.
“A rayuwa, akwai lokacin komai. Lokaci mai zuwa da lokacin tafiya. Na yi imani cewa wannan shine lokacin da zan tafi,” kamar yadda ya shaidawa manema labarai.
“Ina matukar godiya da kyakkyawar tawagar jihara, Abia Warriors, har yanzu ina daya daga cikinsu.”