Mukaddashin gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa, ya koma jihar ne a ranar Laraba, kwanaki biyu bayan ganawarsa da shugaba Bola Tinubu a fadar shugaban kasa dake Abuja.
Aiyedatiwa ya gana da shugaban kasa da wasu masu ruwa da tsaki kan rikicin siyasar jihar Ondo.
Mukaddashin gwamnan wanda ya sauka a filin jirgin saman Akure a cikin wani jirgin sama na kasuwanci, ya samu tarbar wani jigo a jam’iyyar APC da kuma daraktan kula da harkokin kasuwanci na hukumar raya yankin Neja Delta (NDDC), Ifedayo Abegunde.
Ya isa jihar ne jim kadan bayan majalisar ta tabbatar da samun wata wasika daga gwamna Oluwarotimi Akeredolu da ke mika masa mulki.
A cikin wasikar, Akeredolu ya kuma bayyana cewa zai tafi hutun jinya.
Idan ba a manta ba rashin gwamnan ya haifar da dagula al’amura a jihar, inda ake kira da a mika mulki ga Aiyedatiwa kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.
Haka kuma, ci gaban ya haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin mambobin majalisar zartaswar jihar, inda wasu kwamishinonin suka kafa tantuna tare da Aiyedatiwa.
An kuma yi zargin cewa wasu jami’ai na yin jabun sa hannun gwamnan.