fidelitybank

Mataimakin Gwamna ya koma jihar sa ta Ondo a matsyin Gwamna

Date:

Mukaddashin gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa, ya koma jihar ne a ranar Laraba, kwanaki biyu bayan ganawarsa da shugaba Bola Tinubu a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Aiyedatiwa ya gana da shugaban kasa da wasu masu ruwa da tsaki kan rikicin siyasar jihar Ondo.

Mukaddashin gwamnan wanda ya sauka a filin jirgin saman Akure a cikin wani jirgin sama na kasuwanci, ya samu tarbar wani jigo a jam’iyyar APC da kuma daraktan kula da harkokin kasuwanci na hukumar raya yankin Neja Delta (NDDC), Ifedayo Abegunde.

Ya isa jihar ne jim kadan bayan majalisar ta tabbatar da samun wata wasika daga gwamna Oluwarotimi Akeredolu da ke mika masa mulki.

A cikin wasikar, Akeredolu ya kuma bayyana cewa zai tafi hutun jinya.

Idan ba a manta ba rashin gwamnan ya haifar da dagula al’amura a jihar, inda ake kira da a mika mulki ga Aiyedatiwa kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Haka kuma, ci gaban ya haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin mambobin majalisar zartaswar jihar, inda wasu kwamishinonin suka kafa tantuna tare da Aiyedatiwa.

An kuma yi zargin cewa wasu jami’ai na yin jabun sa hannun gwamnan.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran Æ™asa za ka mayar da kai ba zaÉ“en 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp