Matafiya uku ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu biyu suka samu raunuka a ranar Laraba, a hanyar Kaduna zuwa Abuja.
Wani mazaunin kauyen Kakau da ke kan titin Kaduna zuwa Abuja, Malam Nasir Idris ya ce hadarin ya faru ne sakamakon wuce gona da iri.
A cewarsa, hatsarin ya faru ne sakamakon fashewar taya a yayin da motar bas din ta fada wani rami.
Karanta Wannan: Hatsarin mota ya sa gwamnatin Senegal ta bayar da hutu na kwana 3
“Ina cikin gonata da ke kan hanyar Kaduna zuwa Abuja, kwatsam sai na ji karar hayaniya. Yayin da na garzaya wurin tare da wasu mutanen kauye, kura ta fara lulluɓe ko’ina. Da kura ta lafa, gawarwaki uku na kwance.” Inji shi.
Sai dai kwamandan sashin na hukumar kiyaye hadurra ta tarayya, Kaduna ya kasa amsa kiran nasa har zuwa lokacin hada wannan rahoto.