fidelitybank

Mata na tona gidan Tururuwa don neman abinci a jihar Borno

Date:

Mazauna wasu yankunan jihar Borno da ma’aikatan kiwon lafiya, sun nuna fargaba game da ƙaruwar yara masu tamowa da ake samu a cikin jihar.

Abin da suka ce na da nasaba da rashin wadataccen abinci mai gina jiki ga mata masu shayarwa.

Bugu da ƙari rahotanni sun nuna cewa ƙananan hukumomi bakwai ne a jihar ta Borno, matsalar ta fi shafa.

Ƙananan hukumomin sun haɗa da Marte da Kukawa da Abadam da Guzamala da Kaga da Mobar da kuma Gubio.

Yaran da ke a waɗannan ƙananan hukumomin sun dogara ne kacokam ga tallafin da suke samu daga ƙungiyoyin agaji.

Wata mata da ke aiki a ɗaya daga cikin ƙungiyoyin agajin Fatima Muhammed Habib, ta shaida wa BBC cewa, ada mutane basu san ana fama da wannan matsala ba.

Ta ce,” Da muka je ɗaya daga cikin waɗannan garuruwa mun tarar rabin yaran garin na fama da matsalar abinci mai gina jiki, haka suma matan da ke shayarwa, zaka gansu duk a wahale babu wani abinci mai maiƙo ko kyau da suke samu suna ci ga shi kuma suna shayarwa.”

Fatima Muhammed Habib, ta ce idan har uwa bata ci ta ƙoshi ba ta yaya za ta samu ruwan nono ballantana har ta shayar da ɗanta?.

Ta ce,” Saboda tsagwaron yunwa haka zaka ga mata na tona gidan tururuwa don samu abinci, haka mata ke ƙungiya suna yawo don neman gidan tururuwar da za su samu abinci.”

” Babban abin tashin hankalinma shi ne daji matan ke zuwa don su samo gidan tururuwar, ga rashin tsaro a wuraren ga macizai da dai sauransu.”

Ta ce suna kai musu taimako, amma taimakon ba lallai ya isa ba.

Kungiyar likitoci ta Medicins Sans Frontiers ta fitar da wani rahoto a watan Yuni inda ta ce akwai yara 1,594 da ke fama da ƙarancin abinci mai gina jiki.

Gwamnatin jihar dai ta ce tana ƙokari wajen kawo karshen wannan matsala.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp