fidelitybank

Masu ɗaga tutar Rasha a zanga-zanga akwai babbar matsala – Bukarti

Date:

Daruruwan masu zanga-zanga sun bi titunan yawancin jihohin arewacin Najeriya da kuma Legas, a yayin da aka shiga rana ta biyar da fara zanga-zangar kuncin rayuwa a kasar.

An ga wasu masu zanga-zangar sun sake haduwa a wasu bangarori na Abuja da kuma Fatakwal da ke kudancin Najeriya.

A wasu jihohin arewa maso yammacin Najeriyar da suka hada da Zamfara da kuma Kaduna, an samu fitowar masu zanga-zangar da dama a yau Litinin inda har wasunsu ke daga tutar Rasha.

Akwai wasu faifayen bidiyo da aka yada a shafukan sada zumunta da ke nuna yadda wasu masu zanga-zangar ke rike da tutar Rasha tare da nuna damuwa a kan karuwar matsalar tsaro a yankunansu.

Ba a san dalilin kawo Rasha cikin zanga-zangar ba, to amma ana fargabar za a iya bai wa lamarin wata fassara ta daban.

Wasu masu sharhi a Najeriya, kamar Bulama Bukarti, sun yi gargadin cewa yawaitar amfani da tutar Rasha a zanga-zangar akwai babbar matsala.

Cikin shafinsa na X , Bukarti ya ce, “Ina bukatar masu zanga-zangar da su yi taka tsan-tsan,sannan kuma kada su bari wasu masu mummunar manufa su yi amfani da su wajen cimma mummunar manufarsu.”

A ranar Lahadi ne shugaban Najeriyar Bola Tinubu, ya gabatar da jawabi ga ‘yan kasar inda ya yi kira ga masu zanga-zangar kuncin rayuwar da su dakatar, abin da wadanda suka shiryata suka ce shugaban kasar bai tabo batutuwan da suke bukata ba a yayin jawabin nasa abin da ya kara tunzurasu ke nan.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp