fidelitybank

Masu ɓoye abinci a Kano za mu dawo kan ku – Hukumar karɓar ƙorafe-ƙorafe ta Kano

Date:

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa da karbar korafe-korafe ta jihar Kano, ta gargadi ‘yan kasuwar da ake zargi da boye kayan abinci da su daina.

Hukumar ta ce bayan korafe-korafen da ta karba daga mutane daban-daban ta umarci jami’anta su fara bincike wuraren da ake zargin an makare manyan sito-sito da kayan abinci.

Shugaban hukumar Muhuyi Magaji Rimin Gado ya ce sun gano cewar boye kayan na daga cikin abubuwan da suke kara tsadar kayan masarufi a Kano, inda ya ce duk mutumin da suka kama to zai dandana kudarsa.

Ana dai ta zarge-zarge cewa manyan ‘yan kasuwa na boye kayan masarufi har sai ya yi tsada su fito da shi su sayar, wani abu da ake ganin yana taimakawa wajen kara dagula lamarin tsadar kayan na masarufi a Najeriya.

‘Yan kasuwa dai a Kano da ma Najeriya na musanta zarge-zargen da ake yi musu, inda ko a makon da ya gabata sai da gamayyar kungiyar ‘yan kasuwa a birnin Kano ta yi barazanar rufe kasuwanci saboda tsadar abubuwa.

Ko a makon da ya gabata sai da daruruwan al’ummar birnin Minna na jihar Naija suka yi zanga-zangar nuna damuwa kan yanayin tsananin rayuwa da ake ciki.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp