fidelitybank

Masu zuba hannun jari ku ciyar da Najeriya a harkokin makamashi – Shettima

Date:

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima, ya bukaci masu zuba jari na cikin gida da na waje da su ci gajiyar sabbin damammaki da karancin wutar lantarki ya haifar a kasar nan.

Shettima ya yi wannan kiran ne a ranar Litinin din da ta gabata, a wajen bude taron bayar da kudi na mayar da kamfanin samar da wutar lantarki na kasa guda biyar, NIPP, Plants a Abuja.

Mataimakin shugaban wanda ya samu wakilcin mataimakin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa (Ofishin mataimakin shugaban kasa), Sen. Ibrahim Hadejia, ya ce taron ya kasance tabbaci ne ga ‘yan kasuwa da kuma fara saka hannun jari tare da samun riba mai kyau.

Ya jaddada bukatar masu zuba jari su yi amfani da damar da gwamnatin tarayya ke yi na kara zuba jari a bangaren makamashin Najeriya.

Shettima ya kuma yi alkawarin daukar nauyin gwamnatin shugaba Bola Tinubu na magance matsalar karancin makamashi a kasar, inda ya kara da cewa gwamnati ta mayar da hankali wajen inganta harkokin kasuwanci.

“Rashin wutar lantarki a Najeriya yana ba da gayyata ga abokan huldar gida da waje. Muna nan don ƙarfafa ƙoƙarin haɗin gwiwa don samar da mafita mai dorewa.

“Gwamnati ta tsaya tsayin daka wajen magance karancin makamashi kuma ta mai da hankali kan inganta saukin kasuwanci.

Mataimakin shugaban kasar, duk da haka, ya bukaci masu son zuba jari da su “dauki nauyin amana wajen amfani da wadannan albarkatun domin amfanin kasa,” in ji shi.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp