Magoya bayan Gwamna Sim Fubara sun mamaye gidan gwamnatin jihar Ribas.
Kungiyar tana kira ga Ministan Babban Birnin Tarayya da ya bar Gwamnan ya yi aikinsa a matsayinsa na Shugaban zartarwa na Jihar.
Wike da dan takararsa da aka zaba a zaben gwamna a 2023 sun yi kaca-kaca, inda a karshen makon da ya gabata cece-ku-ce a tsakaninsu ya rikide zuwa fafutukar neman ballewa daga Fubara da gwamnatinsa.
An samu baraka a tsakanin ‘yan majalisar dokokin jihar Ribas a ranar Lahadin da ta gabata yayin da wasu daga cikinsu suka fara shirin tsige Gwamna Fubara.
Edison Ehie, shugaban majalisar dokokin jihar, ya ki amincewa da yunkurin tsige gwamnan, bai aikata wani laifin da za a iya tsige shi ba, saboda haka aka cire shi a matsayin shugaban masu rinjaye.
Daga baya an zabi Edison a matsayin kakakin majalisar dokokin jihar Ribas.
Wasu daga cikin masu zanga-zangar da suka zanta da manema labarai, sun yi mamakin dalilin da yasa tsohon gwamnan zai so a ce ya ci gaba da mulkin jihar da ya yi mulki na tsawon shekaru takwas.