Masu zanga-zanga a Bangladesh, sun ci gaba da afka wa gine-gine masu alaƙa da iyalan tsohuwar firaiministar ƙasar Sheikh Hasina wadda aka hamɓarar da gwamnatinta a shekarar da ta gabata tare da cinna wuta.
Daruruwan mutane yawancinsu dalibai ne suka yi amfani da ƙananan motocin ruguza gine-gine wajen farfarasa abubuwa da farwa gidan mahaifin tsohuwar firaiministar, Sheikh Mujibur Rahman, wanda shi ne shugaban ƙasar na farko, bayan samun ‘yancin kan ƙasar daga Pakistan.
Haka kuma masu zanga-zangar sun lalata gidajen biyu daga cikin ƙusoshin jam’iyyar tsohuwar firaministar, tare da cire allunan da ke ɗauke da sunanta ko na danginsu daga jami’ar ƙasar da ke birnin Rajshahi.
Zanga-zangar ta ɓarke ne bayan da aka samu labarin Sheikh Hasina za ta yi wa magoya bayanta jawabi ta shafin sada zumunta daga Indiya, inda ta gudu bayan hamɓarar da ita a watan Agustan bara.