Gwamnatin jihar Kano ta ce, bata-garin da suka afka wa babbar kotun jihar yayin zanga-zanag kan tsadar rayuwa sun kwashe takardun tuhumar da ake yi wa tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje kan cin hanci da rashawa.
Ganduje ne shugaban jam’iyyar APC na Ć™asa mai mulkin Najeriya a yanzu bayan ya mulki Kano tsawon shekara takwas a Ć™rĆ™ashin jam’iyyar.
“Abin takaici ne a ce wasu maĆ™iyan Kano sun É—auko hayar wasu domin lalata gine-gine masu tarihi da zimmar kare tsohon Gwamna Ganduje da iyalansa daga shari’ar cin hanci,” a cewar Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf lokacin da ya kai ziyara kotun a ranar Laraba.
Gwamnatin Kano Ć™arĆ™ashin jam’iyyar NNPP na tuhumar Ganduje, da matarsa Hafsat, da É—ansa Umar, da wasu mutum biyu bisa zargin karkatar da biliyoyin kuÉ—aÉ—e a lokacin mulkinsa.
Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sanusi Bature, ya fitar ta Ć™ara da cewa masu zanga-zanagr sun lalata “kusan kowane É“angare na kotun da jawo asarar sama da naira biliyan É—aya” ta hanyar sace kayayyaki, da Ć™ona motoci.