fidelitybank

Masu zanga-zanga sun bukaci EFCC ta sake tuhumar Matawalle

Date:

Masu zanga-zanga daga jihar Zamfara a ranar Juma’a sun mamaye kofar shiga hedikwatar hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC.

Suna rokon hukumar yaki da cin hanci da rashawa da ta sake bude bincike kan tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle.

A cewar gidan talabijin na Channels, masu zanga-zangar a karkashin inuwar jam’iyyar APC Loyalists Forum na son hukumar EFCC ta binciki duk wasu korafe-korafen da ake yi wa tsohon gwamnan.

Hakan ya hada da karkatar da kwangilar da ake zargin ta kai har naira biliyan 70 a lokacin yana gwamnan jihar.

An ce Daraktan Hulda da Jama’a na EFCC, Wilson Uwujaren ne ya karbi takardar zanga-zangar a madadin shugaban.

Ya kuma tabbatar wa masu zanga-zangar cewa EFCC ta kuduri aniyar bin duk wata shari’a ta cin hanci da rashawa domin cimma matsaya mai ma’ana.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp