Ministan babban birnin tarayyar Abuja, Nyesom Wike ya shawarci masu zanga-zangar da su killace ayyukansu a filin wasa na Moshood Abiola, domin bin umarnin da kotu ta bayar.
Ya ba da shawarar ne a Abuja yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan ya gudanar da wani taron gaggawa da shugabannin hukumomin tsaro na birnin.
Ministan wanda ya amince da Æ´ancin yin zanga-zanga a tsarin dimokradiyya ya ce dole a gudanar da irin wannan zanga-zangar kamar yadda doka ta tanada.
Ya ce, “Mun yi imanin cewa wannan gwamnatin dimokradiyya ce don haka dole ne mu yi mulki bisa ƙa’ida.
“Mun kuma yi imanin cewa masu zanga-zangar suna yi ne saboda hakkinsu ne, amma ya kamata su gudanar da zanga-zangar ta yadda gwamnati za ta samu damar warware masu matsalolinsu.”
Ya ce jami’an tsaro za su ƙyale masu zanga-zangar su yi taro a filin wasan, inda ya ce ƴan jarida za su kasance a wurin domin isar da sakon su ga gwamnati da sauran ƙasashen duniya.