Kwana uku kenan da shirin gudanar da zanga-zangar a fadin kasar nan, kwamandan hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara, Umar Mohammed, ya gargadi masu zanga-zangar da da su gujewa aikata miyagun laifuka tare da haddasa tarzoma a jihar.
Ya yi wannan gargadin ne a ranar Litinin a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan Ayoola Michael Shola ya fitar a Ilorin.
Umar ya bayyana cewa rundunar tana cikin shirin ko ta kwana, tare da daukar kwararan matakai na tabbatar da bin doka da oda kafin muzaharar, da lokacin da kuma bayan zanga-zangar.
Ya kuma kara da cewa rundunar ba za ta nade hannayenta tana kallon ‘yan iska suna barna, da barnata muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa ba, domin za a samar da isassun kayan aiki a fadin jihar domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.
Yayin da yake amincewa da ‘yancin ‘yan kasa na gudanar da zanga-zangar, kwamandan Umar, ya bukaci matasa da sauran ‘yan kasa da su bayyana kokensu bisa doka da lumana, tare da tabbatar da cewa tsaron kasa da lafiyar jama’a ba su taka kara ya karya ba.
Ya kuma ja kunnen Kwaran masu bin doka da oda da su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum ba tare da tsoro ba, yana mai tabbatar da cewa an dauki tsauraran matakai don tunkarar barazanar da ake shirin yi.