fidelitybank

Masu zanga-zanga ku guji haddasa rikici a Kwara – NSCDC

Date:

Kwana uku kenan da shirin gudanar da zanga-zangar a fadin kasar nan, kwamandan hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara, Umar Mohammed, ya gargadi masu zanga-zangar da da su gujewa aikata miyagun laifuka tare da haddasa tarzoma a jihar.

Ya yi wannan gargadin ne a ranar Litinin a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan Ayoola Michael Shola ya fitar a Ilorin.

Umar ya bayyana cewa rundunar tana cikin shirin ko ta kwana, tare da daukar kwararan matakai na tabbatar da bin doka da oda kafin muzaharar, da lokacin da kuma bayan zanga-zangar.

Ya kuma kara da cewa rundunar ba za ta nade hannayenta tana kallon ‘yan iska suna barna, da barnata muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa ba, domin za a samar da isassun kayan aiki a fadin jihar domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.

Yayin da yake amincewa da ‘yancin ‘yan kasa na gudanar da zanga-zangar, kwamandan Umar, ya bukaci matasa da sauran ‘yan kasa da su bayyana kokensu bisa doka da lumana, tare da tabbatar da cewa tsaron kasa da lafiyar jama’a ba su taka kara ya karya ba.

Ya kuma ja kunnen Kwaran masu bin doka da oda da su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum ba tare da tsoro ba, yana mai tabbatar da cewa an dauki tsauraran matakai don tunkarar barazanar da ake shirin yi.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp