fidelitybank

Masu zanga-zanga a Kenya sun yi barazanar tsige shugaban ƙasa

Date:

A yau, Alhamis, matasan Kenya suka ci gaba da zanga-zangar da suka fara ta ƙin jinin gwamnati, wadda ta faro sanadiyyar ƙin yarda da ƙarin haraji, wadda ta rikiɗe zuwa buƙatar shugaban ƙasar William Ruto ya yi murabus daga muƙaminsa.

Masu shirya zanga-zangar sun yi barazanar yin tattaki har zuwa fadar shugaban ƙasar da nufin “tsige Shugaba William Ruto,” a cewar wani rahoto da gidan talabijin na Citizen TV mai zaman kansa ya fitar.

Ɗaya daga cikin manyan masu jagorantar zanga-zangar, Kasmuel McOure, ya bayyana zanga-zangar ta yau a matsayin “mafi girman zanga-zanga a cikin duk zanga-zangar da aka yi a ‘yan kwanakin nan,” a wata hira da Citizen TV.

Matasan sun shafe wata uku suna gudanar da zanga-zangar da tuni ta tilasta wa gwamnati janye ƙudirin ƙarin harajin da kuma rusa majalisar ministocin ƙasar.

Jaridar Capital News ta ba da rahoton gagarumin gangami a shafukan sada zumunta, tare da yin kiraye-kiraye a mamaye cibiyoyin gwamnati don nuna adawa da “mummunan shugabanci.

A martanin da ya mayar, Shugaba Ruto ya yi gargaɗi game da tashe-tashen hankali, yana mai jaddada ƙudurin ƙasar na samar da zaman lafiya.

Zanga-zangar ta yau ta zo daidai da rantsar da sabuwar majalisar ministocin Shugaba Ruto, wadda ta ƙunshi ‘yan siyasa hudu na adawa.

Sai dai masu zanga-zangar sun ƙi amincewa da sabuwar majalisar ministocin, saboda shigar da tsofaffin ministocin da ake zargi da “rashin ƙwarewa da rayuwa ta wadaƙa.”

haka kuma akwai wani ƙudurin doka da ke gaban majalisar dokokin ƙasar, wanda idan an zartar da shi, zai dora alhakin duk wata ɓarna a lokacin zanga-zanga kan masu shiryata.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp