fidelitybank

Masu zanga-zanga a Kano sun ce ba gudu ba ja da baya

Date:

Wasu ƙungiyoyi da ke shirin jagorantar zanga-zanga a Najeriya, sun fito sun bayyana kansu a wani taro da suka gudanar a jihar Kano a ranar Talata.

Gamayyar ƙungiyoyin daga arewacin Najeriya sun jaddada cewa ba gudu ba ja da baya za su fito zanga-zangar da suka ce za su jagoranta a sassan arewacin kasar, duk da gargaɗi da roƙon gwamnati su ƙara haƙuri su jingine zanga-zangar.

Ƙungiyoyin sun shirya gudanar da zanga-zangar ta kwana 10 daga ranar Alhamis 1 ga Agusta.

Sun ce zanga-zanga ita ce kawai zaɓin da ya rage masu domin nuna fushinsu kan halin da Najeriya ke ciki na matsalolin tattalin arziki da tsaro.

Amma hukumomin gwamnati na ci gaba da gargaɗin yiyuwar tashin hankali kuma wasu na iya amfani da zanga-zangar su wawushe dukiyoyin al’umma.

Farashin kayan masarufi a Najeriya sun yitashin gauron zabi da ba a taɓa gani ba a tarihi, ɗaya daga cikin dalilin da ke ingiza zanga-zangar da ta ja hankali a shafukan sada zumunta.

Masu shirin jagorantar zanga-zangar kuma yanzu sun fito sun faɗi dalilansu da kuma buƙatu da yadda suka tsara gudanar da zanga-zangar.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp