fidelitybank

Masu zanga-zanga 8 sun mutu a Kenya

Date:

Aƙalla masu zanga-zangar nuna adawa da ƙarin haraji a Kenya 8 ne aka tabbatar da mutuwarsu a birnin Nairobi bayan da suka mamaye harabar majalisar jim kadan bayan da ‘yan majalisar suka amince da sabon tsarin ƙrin haraji, a cewar wani rahoto da gidan talabijin ta KTN TV mai zaman kanta ta fitar.

Gidan talabijin ɗin ya ruwaito cewa mutane da dama sun jikkata sakamakon hargitsin da ya biyo baya yayin da ‘yan sanda suka yi yunkurin hana masu zanga-zangar shiga harabar majalisar.

Hotunan bidiyo da aka yi ta watsawa a shafukan sada zumunta sun nuna gawarwakin mutane da kuma mutanen da suka jikkata yayin zanga-zangar.

Rahotanni sun ce ‘yan sandan sun yi amfani da hayaki mai sa hawaye domin daƙile masu zanga-zangar da suka mamaye majalisar.

An kuma ƙona wani ɓangare na ginin majalisar.

Kafofin yada labaran cikin gida sun kuma bayar da rahoton cewa an kwashe ƴan majalisar cikin gaggawa zuwa wasu gine-ginen da ke kusa.

Matasan Kenya ne dai suka jagoranci zanga-zangar neman a janye kudirin kasafin kudin shekarar 2024, wanda ya gabatar da sabbin ƙarin ƙudin haraji.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp