Akalla mutane shida ne rahotanni suka ce sun mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata a wata zanga-zangar da ake ci gaba da yi a garin Suleja na jihar Neja.
Lamarin dai ya faru ne a daidai lokacin da jamiāan tsaro suka yi yunkurin tarwatsa gungun masu zanga-zangar da suka yi shingen shinge a wani sashe na hanyar Abuja zuwa Kaduna, lamarin da ya haifar da cikas ga cunkoson ababen hawa tare da kama fasinjoji da masu ababen hawa na tsawon saāoāi.
Daga cikin wadanda suka mutu har da Yahaya Nda Isah, wani mazaunin titin Hassan Dalatu, Suleja, wanda harsashi ya same shi a lokacin da yake kan babur dinsa a gaban rundunar āyan sandan Suleja āAā, inda masu zanga-zangar suka taru. Wani dan uwa ga Isah ya bayyana cewa kawun nasa baya shiga zanga-zangar amma yana wucewa ne kawai sai wani harsashi da ya bata a kirji ya same shi.
āShi ne kawuna. Bai ko yi zanga-zanga ba. Yana wucewa ne a gaban sashin āAā na āyan sanda inda wasu mutane ke zanga-zangar sai harsashi ya same shi a kirjinsa, kuma ya mutu. Yayin da nake magana da ku, ina cikin gidansa tare da sauran makoki. Abin takaici ne,ā in ji shi.
Wani da lamarin ya shafa mai suna Malam Abu shi ma ya rasu a nan take. Shaidu sun ce an harbe wasu mutane uku a wuri guda, sannan an harbe wasu biyu a mahadar Suleja da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, duk da cewa ba a iya tabbatar da halin da suke ciki.
Zanga-zangar dai ta yi kamari inda aka tura karin jami’an tsaro domin shawo kan lamarin. Mazauna yankin sun bayyana lamarin a matsayin tashin hankali, inda aka shafe kusan mintuna 20 ana jin karar harbe-harbe a dandalin mai martaba sarkin, lamarin da ya sa da dama suka tsere domin tsira da rayukansu.
Wani mai shago mai suna Bala Abdullahi ya bayyana cewa, āMun ji mutane suna ihu, an kuma rika jin karar harbe-harbe na tsawon mintuna 20 a wajen dandazon sarki. Alāamarin Suleja ya yi muni.ā
Kakakin Rundunar āYan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da cewa wasu āyan iska sun yi yunkurin kona karamar hukumar Tafa, amma jamiāan tsaro sun tarwatsa su. Ya bada tabbacin cewa an share hanyar Kaduna da kuma gate din karban kudi.
āāYan bata-gari sun yi yunkurin bankawa karamar hukumar Tafa wuta, āyan sanda da sojoji sun tarwatsa su. An share hanyar Kaduna da gate din karba,ā inji shi.
Da aka tuntube shi don Ęarin bayani, Wasiu Abiodun ya ce, “Bari in tabbatar kuma in dawo gare ku.”