Hukumar kula da masu yi wa kasa hidima ta Najeriya (NYSC), ta kaddamar da shirinta na shigar da masu hidimar cikin tsarin inshorar kula da lafiya na kasa.
A shirin wanda aka kaddamar yau Juma’a 11 ga watan Fabrairu 2022, a shelkwatar hukumar da ke Abuja, masu hidimar za su rinka cin moriyar kula da lafiyarsu daga lokacin da matashi ya karbi takardarsa ta zuwa sansanin horo zuwa sati uku, bayan kammala aikin na kasa.
Domin tabbatar da shirin na tafiya yadda ya kamata, hukumar ta NYSC ta ce ta zabi asibitoci shida daga shiyyoyi shida na kasar domin gudanar da shi.
Hukumar ta bukaci matasan da ke cikin aikin bautar kasar da su je su yi rijista da asibitocin da ke yankunan da suke aikin. A cewar BBC.
Shugaban hukumar ta NYSC, Manjo Janar Shuaibu Ibrahim, ya ce, kaddamar da shirin kula da lafiyar cika umarnin da shugaban kasa ya bayar ne a shekara ta 2016, wanda ya biyo bayan kisan da aka yi wa wasu masu yi wa kasa hidima uku da aka tura sansanonin horon aikin a jihohin Kano da Zamfara da kuma Bayelsa.